Gwamna Matawalle na Shirin rushe sakatariyar Jam’iyyar PDP a Zamfara

Date:

Daga Maryam adamu Mustapha
Jam’iyyar PDP ta ce ta shigar da kara tana kalubalantar Hukumar Tsara Birane ta Zamfara, ZUREP, kan batun rushe sakatariyar jam’iyyar ta jihar a Gusau.
 Bala Mande, shugaban riko na jihar ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron Masu Ruwa da tsaki jam’iyyar a sakatariyar ranar Laraba.
 Bala Mande, wanda tsohon shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin zamfara ne Lokacin Bello Matawalle yace sanya alama a sakatariyar jam’iyyar domin rushe ta ba dai-dai ba ne kuma wani yunkuri ne na kuntatawa ‘ya’yan jam’iyyar ta PDP a zamfara.
 “’ya’yan jam’iyyar PDP ‘yan kasa ne masu bin doka da oda, kuma mun tunkari kotun da ta dace domin neman hakkinmu kan lamarin.
 Shugaban rikon jam’iyyar PDPn, wanda Kanar mai ritaya ne, ya bukaci magoya bayan jam’iyyar PDP da su ci gaba da bin doka da oda, kuma su guji daukar doka a hannunsu.
 Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa ya rawaito cewa, a karar da aka shigar a gaban babbar kotun Zamfara da ke zamanta a Gusau, jam’iyyar PDP na daga cikin wadanda ke neman kotu ta yi watsi da Shirin  rushe sakatariyar jam’iyyar da ZUREP ke Shirin yi, Inda tasa alama tun a ranar 29 ga watan Oktoba tare da bayyana ginin sakatariyar a matsayin haramtacce.
Kadaura24 ta rawaito Gwamnan Jihar zamfara Bello Matawalle Bai Dade da barin jam’iyyar ta PDP ba ,Inda ya Koma jam’iyyar APC tun a Watan yuli Wannan Shekara.

18 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...