EFFC tace bata Sami Rigar Mama ta Gwal Cikin kadarorin Diezani ba

Date:

Shugaban hukumar yaƙi da rashawa a Najeriya (EFCC) ya musanta rahotannin da ke yawo cewa akwai rigar mama ta gwal a cikin kayan da hukumar ta ƙwace daga hannun Diezani Alison-Madueke, tsohuwar ministar man fetur ta Najeriya.

Ana zargin Diezani wadda ta fice daga Najeriya a 2015 da satar kuɗin da suka kai dala biliyan biyu da rabi daga asusun gwamnatin ƙasa a lokacin da take minista, kodayake ta musanta zargin.

A watan Mayu ne Shugaban EFCC Abdulrasheed Bawa ya faɗa wa Majalisar Wakilai cewa darajar sarkoki da awarwaro da sauran kayan ƙawa da aka ƙwace daga wurin Diezani ta kai naira biliyan 14.

A watan Oktoba gwamnatin tarayya ta lissafa wasu kadarorinta da ta ƙwace waɗanda suka haɗa da gidaje a Banana Island da ke Ikoyi ta Jihar Legas.

Sai dai da ya bayyana a kafar talabijin ta TVC ranar Laraba, Abdulrasheed Bawa ya ce labarin rigar mama ta gwal da aka ce akwai ta a cikin kayan na ƙanzon kurege ne.

Babu wani abu mai kama da rigar mama ta gwal, maganar ‘yan kafafen sada zumunta ce,” in ji shi.

“Zan iya faɗa muku a kyauta saboda ni ne jagoran wannan binciken. Ban san da ita ba. Idan da akwai ta ya kamata a ce na sani. Ya kamata na sani saboda ni na jagoranci binciken da sauransu.”

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...