INEC ta bayyana matsalolin da aka samu a zaɓen jihar Anambra

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya Inec ta ce an samu matsaloli da suka kawo cikas ga harkokin zaɓen gwamnan jihar Anambra.

Hukumar ta kuma amince da cewa wasu na’urorin tantance masu zaɓe sun samu matsala yayin da ta kasa tura jami’anta a wasu wuraren, kamar yadda shugaban hukumar a Anambra Nkwachukwu Orji ya shaida wa manema labarai.

Ya ce hukumar za ta yi amfani da dokoki da tsarinta na karɓar sakamakon zaɓe.

BBC Hausa ta rawaito Shugaban hukumar ya ce inda aka samu matsala za a iya tattara sakamakon a cibiyoyin tattara sakamako na ƙananan hukumomi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya gabatar da kasafin kudin 2026 da ya kai N1.368 tiriliyan

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya gabatar...

Nazarin Yadda Shaharar Sanata Barau Ta Karade Nigeria – Abba Anwar

Daga Abba Anwar Wani babban abin lura game da rayuwar...

Kungiyar Ɗaliban Mariri ta gudanar da aikin duba marasa Lafiya kyauta a yankin

Daga Abdallahi Shu'aibu Hayewa   Kungiyar Dalibai ta Makarantar Mariri wato...

Gwamnan Taraba ya bayyana dalilinsa na shirin komawa APC

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ce zai shiga...