INEC ta bayyana matsalolin da aka samu a zaɓen jihar Anambra

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya Inec ta ce an samu matsaloli da suka kawo cikas ga harkokin zaɓen gwamnan jihar Anambra.

Hukumar ta kuma amince da cewa wasu na’urorin tantance masu zaɓe sun samu matsala yayin da ta kasa tura jami’anta a wasu wuraren, kamar yadda shugaban hukumar a Anambra Nkwachukwu Orji ya shaida wa manema labarai.

Ya ce hukumar za ta yi amfani da dokoki da tsarinta na karɓar sakamakon zaɓe.

BBC Hausa ta rawaito Shugaban hukumar ya ce inda aka samu matsala za a iya tattara sakamakon a cibiyoyin tattara sakamako na ƙananan hukumomi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...