An Kama Malamin Islamiyyar da ya sace dan uwansa a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ta ce ta kama wani malamin makarantar Islamiyya bisa zargin sace dan dan uwansa domin karbar kudin fansa.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba ta hannun kakakinta, SP Gambo Isah, rundunar ta ce ta kama malamin mai suna Jamilu Idris da ke karamar hukumar Faskari bisa zargin sace dan dan uwansa, Umar Farouk Kabir, dan shekara hudu.

A cewarta, ranar 9 ga watan jiya Jamilu ya je gidan dan uwansa, Kabiru Abdullahi a Funtua ya sace dansa zuwa garin Dutsen-Alhaji da ke Abuja, babban birnin kasar.

BBC Hausa ta rawaito Rundunar ta ce daga nan ne Jamilu ya kira yayan nasa ya bukaci ya bayar da kudin fansa da suka kai naira miliyan biyar.

Ta kara da cewa mutumin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya gabatar da kasafin kudin 2026 da ya kai N1.368 tiriliyan

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya gabatar...

Nazarin Yadda Shaharar Sanata Barau Ta Karade Nigeria – Abba Anwar

Daga Abba Anwar Wani babban abin lura game da rayuwar...

Kungiyar Ɗaliban Mariri ta gudanar da aikin duba marasa Lafiya kyauta a yankin

Daga Abdallahi Shu'aibu Hayewa   Kungiyar Dalibai ta Makarantar Mariri wato...

Gwamnan Taraba ya bayyana dalilinsa na shirin komawa APC

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ce zai shiga...