An Kama Malamin Islamiyyar da ya sace dan uwansa a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ta ce ta kama wani malamin makarantar Islamiyya bisa zargin sace dan dan uwansa domin karbar kudin fansa.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba ta hannun kakakinta, SP Gambo Isah, rundunar ta ce ta kama malamin mai suna Jamilu Idris da ke karamar hukumar Faskari bisa zargin sace dan dan uwansa, Umar Farouk Kabir, dan shekara hudu.

A cewarta, ranar 9 ga watan jiya Jamilu ya je gidan dan uwansa, Kabiru Abdullahi a Funtua ya sace dansa zuwa garin Dutsen-Alhaji da ke Abuja, babban birnin kasar.

BBC Hausa ta rawaito Rundunar ta ce daga nan ne Jamilu ya kira yayan nasa ya bukaci ya bayar da kudin fansa da suka kai naira miliyan biyar.

Ta kara da cewa mutumin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...