Bani na kirawo su Malam Shekarau da Banza 7 ba – Ganduje

Date:

Daga Halima M Abubakar

Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje yace ba shi bane ya kirawa ayarin su Malam Ibrahim Shekarau a Matsayin Banzan bakwai ba.
Gwamnan ya bayyana hakan ne Cikin Wata Maganawa da sukai da Sashin Hausa na Radio Faransa.
Ganduje yace Wani ne ya tambayi Cewa Wadancan da basa tare da Gwamnati su nawa ne? sai aka ce Masa su Bakwai ne ,to shi ne ya kirawo su da Sunan Banza bakwai.
” Gwamna bai cewa kowa banza bakwai wani ne ya fada ,Amma ba ni ba” inji Ganduje
Da aka tambaye shi ko zasu bude Kofar sulhu da su Malam Ibrahim Shekarau ?
Ganduje yace Kofa abude take za’a nemi su Wadancan Sanatoci guda 2 da Yan Majalisu 4 da suke ganin ba’a kyuata musu a APC domin aga ta hanayar da za’a warware Matsalolin don a tafi tare gaba daya.
Kadaura24 ta rawaito Rikicin cikin gida ya barke tsakanin Tsohon Gwamnan Kano Kuma Sanatan Kano ta tsaki Malam Ibrahim Shekarau da wasu Yan Majalisu Saboda abun da suka kirawa Rashin adalci da ake yi musu har Suka Kai Kara ga uwar jam’iyyar APC ta Kasa.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...