Shugaba Buhari ya taya Sanata Bashir Lado Murnar Cika Shekaru 55 a Duniya

Date:

 

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya aike da sakon taya murna ga tsohon Babban Darakta na Hukumar Hana Safarar Mutane, Sanata Basheer Garba Lado, bisa zagayowar ranar haihuwarsa, 16 ga Oktoba, 2021, inda jigon jam’iyyar ya cika shekara 55 a duniya.

Shugaba Buharin ya taya Murnar ne Cikin Wata sanarwa da Babban Mai taimaka Masa na Musamman kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya aikewa Manema labarai.

 

Shugaban Kasar ya shiga sahun mambobin Jam’iyyar All Progressives Congress (APC), iyalan sanatan da abokan arzikinsa wajen taya shi murnar cika shekarar ne bisa la’akari da gudunmawarsa wajen cigaban kasa tun daga kuruciyarsa a matsayin dan kasuwa da kuma makaman da ya rike.

 

Bugu da kari, Shugaba Buhari ya yaba wa tsohon dan majalisar, wanda kuma ya taba rike mukamin Kwamishinan a Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira, bisa sadaukarwarsa, da’arsa da mayar da hankalinsa da aka gani kuru-kuru a lokacin da ya ke Majalisar Dattawa da kuma jagoranci nagari da ya bayar a hukumomin da ya rike.

 

Sai Shugaban Kasar ya yi addu’ar Allah ya kara wa sanatan lafiya, ya kuma albarkaci iyalinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...