Rikicin APC :Muna kokarin Sasantawa tsakanin mu da su Mal Shekarau – Sanata Kabiru Gaya

Date:

Daga Usman Aliyu

Sanatan Kano ta kudu Sanata Kabiru Ibrahim Gaya ya bayyana cewa Suna iya bakin kokarin su domin Sasantawa tsakanin Masu goyon bayan jam’iyyar APCn Kano da Kuma bangaren su Sanata Malam Ibrahim Shekarau .

Kadaura24 ta rawaito Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne yayin taron Manema labarai da Yan Majalisu 20 da shi Sanatan suka Shirya don mayar da martani ga korafin da su Sanata Malam Ibrahim Shekarau suka mikawa uwar jam’iyyar ta Kasa.

Sanata Kabiru Gaya yace sun rubuta wasikar martani ga uwar jam’iyyar ta Kasa mai dauke da sa hannu yan Majalisar wakilai 20 da Kuma Sanata guda 1, Inda a ciki wasikar Suka ce babu wani rikici a jam’iyyar APC a Kano Kamar yadda daya bangaren suka ambata a wasikarsu.

Yace duk wani Mataki da Gwamna Ganduje zai dauka a jam’iyyar APC ta jihar Kano sai ya tuntubi duk masu ruwa da tsaki a jam’iyyar, yace Ganduje bai taba daukar Wani Mataki ba tare da sanin mu ba.

“Karkashin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje an gudanar da zaben Shugabanin jam’iyyar a matakan mazabu 484 da Kananan Hukumomi 44 lami lafiya ba tare da Wata matsala ba, don haka ba dai-dai bane ace wai ba’a yi sahihin Zabe ba a Kano.” Inji Kabiru Gaya

“Wadancan Masu korafin Yan uwanmu ne don haka muke Kira a garesu da su Zo mu hada hannu waje guda domin Samun Nasara Jam’iyyarmu ta APC a Zabe Mai zuwa”. Sanata Gaya

Sanata Gaya ya bayyana cewa suna Sanar da uwar jam’iyyar ta Kasa karkashin jagorancin Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni Cewa babu wani rikici a jam’iyyar Kuma Suna tare da jagorancinsa da Shugaban Kasa Muhd Buhari da Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje don haka suke Kira da Shugabanci da yayi watsi da waccen takardar koke da Wasu tsiraru cikinsu Suka rubuta.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarki Aminu Ado Bayero ya baiwa Alan Waka Sabuwar Sarauta a Masarautar Kano

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Mai martaba Sarkin Kano na 15...

Soke Hawan Sallah: Dole Gwamnatin tarayya ta biya mu diyya – Gwamnatin Kano

Daga Isa Ahmad Getso   Gwamnatin jihar Kano ta bukaci gwamnatin...

NiMet ta bayyana jihohin da za a sami tsawa da ruwan sama na kwanaki 3 a Nigeria

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya ta...

Hajjin bana: Gobarar ta tashi a otel din wasu Alhazan Nigeria a Makka

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Hukumar kula da Alhazai ta Najeriya...