2023 :Majalisa ta Amince INEC tayi Amfani da Yanar Gizo Wajen tura Sakamakon Zabe

Date:

Bayan jan kafa na wani tsawon lokaci da matsin lamba, yanzu majalisar dattawan Najeriya ta amince hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC ta yi amfani da na’ura domin aika sakamakon zaɓe.

Majalisar ta sauya ra’ayinta na farko inda ta ƙi amincewa da matakin game da tura sakamakon zaɓe daga muzaɓu ta hanyar intanet.

A zaman da ta yi na ranar Talata, majalisar dattawan ta ce INEC za ta iya amfani da na’ura ta aika sakamakon zaɓe a lokacin da ya dace idan har hukumar kula da harakokin sadarwa ta Najeriya NCC ta amince.

Majalisar ta kuma kaɗa kuri’ar amincewa da tsarin gudanar da zaɓen fidda ƴan takara na jam’iyyu ta hanyar zaɓe kai tsaye tare da sa idon hukumar INEC.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...