Sarkin Kano ya Zama Uban Jami’ar Al-Istiqama ta Sumaila

Date:

Daga Khadija Abdullahi Umar

An nada Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a matsayin uban jami’ar Al-Istiqama dake garin Sumaila a jihar Kano.

Shugaban Jami’ar Hon. Abdulrahman Kawu Sumaila ne ya gabatar da takardar nadin ga Mai Martaba Sarkin Kano a ranar Larabar nan.

Da yake mika takardar ga Mai Martaba sarkin Kawu Sumaila yace sun yi la’akari da kwarewa kogewa da Sarkin yake dasu tare da kokarin da yake yi wajen inganta harkokin Ilimi a jihar Kano da Kasa baki daya.

A Jawabinsa Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya nuna farin Cikinsa tare da bada tabbacin Zai yi duk mai yiwuwa wajen cigaban Jami’ar dama Ilimi baki daya.

Mai martaba sarkin ya bukaci mawadata dake cikin al’umma da su mai da hankali wajen bada tasu Gudunmawar don cigaba Ilimi a Kano da Kasa baki daya

23 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...