Marayu 100 a kano sun rabauta da Tallafin Naman Sallah daga Falakin Shinkafi

Date:

 

Kimanin Marayu 100 sun Amfana da tallafin Naman Sallah da Barka da Sallah a unguwar Yakasai Daga Wani Dan Kasuwa Kuma Dan kishin Kasa Ambasada Yunusa Yusuf Hamza ( Falakin Shinkafi).

Da yake Zantawa da Wakilin Kadaura24 Jim kadan bayan kammala rabon Falakin Shinkafin Amb. Yunusa Yusuf yace ya tallafawa marayun ne domin Sanya farin Ciki a zukatansu a Wannan Lokaci na Sallah Babba.

Yace Marayu Suma’ya’yane da ya kamata a Rika kula dasu Musamman a Lokaci irin Wannan domin a dauke musu radadin Rashin Iyayen su.

Amb. Yunusa Yusuf yace ya Zama wajibi mawadata su Rika tallafawa marayu don kyautata Rayuwar su, “Idan ba’a taimaki Rayuwar su ba hakan ce take sawa su taso basa tausayi Kuma su zamo gurbatattu Saboda da Suma ba’a taimaki Rayuwar suba.

” Ina Amfani da Wannan dama wajen Kira ga Shugabanni da mawadata dasu Rika tallafawa marayu don inganta Rayuwar tare da Samun lada Mai yawa a wajen Allah”. Inji Falakin Shinkafin

Wasu Daga Cikin Iyayen Marayun da Suka Amfana da tallafin sun yabawa Ambassador Yunusa Yusuf Hamza (Falakin Shinkafin) bisa tallafin da ya Baiwa ya’yansu, Inda Suka ce dama ya saba gudanar da irin Wannan tallafi ta karkashin Kungiyar Yakasai Zumunta.

Kadaura24 ta rawaito bayan Naman Sallah Marayun sun rabauta da kudi da Kayan more Rayuwa don faranta musu a Wannan Lokaci na Sallah.

98 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...