Al’ummar kaduna na kokawa da rusan El-Rufa’i

Date:

Mazauna unguwar Malali sun wayi garin Lahadi cikin ɓaraguzan rukunin gidaje da ke Malali Low-Cost sakamakon rusau da gwamnatin Jihar Kaduna ta yi.

Bayanan da BBC Hausa ta tattara sun nuna cewa da misalin ƙarfe 11:30 na daren Asabar ne jami’an tsaro suka isa unguwar da ke ƙwaryar birnin Kaduna, inda suka fara rushe gine-ginen.

Wani mazaunin unguwar mai suna Titus Katuka ya ce tun shekarar 1976 suke haya a gidajen waɗanda mallakar gwamnatin jihar ne amma a 2017 gwamnatin Nasir El-Rufai ta ce za ta sayar musu da su.

Ya ce lokaci guda kuma gwamnatin ta ce za ta rushe su domin gina kasuwa a wurin bayan ta mayar wa da waɗanda suka fara biya kuɗaɗensu, abin da ya sa suka kai ƙara kotu.

“Ni ba a zo kan layinmu ba amma ban sani ba gobe ko jibi za su iya ƙarasowa,” in ji shi.

An gina rukunin gidajen na Malali Low-Cost ne domin masu ƙaramin ƙarfi.

Rushe-rushen na daren jiya Asabar sun shafi rukunin gidaje ne da ke kan layukan Gambia da Siera Leon na unguwar.

Kazalika mutanen sun ce jami’an tsaro sun harba musu hayaƙi mai sa hawaye kafin fara aikin rusau ɗin.

Wasu hotuna da aka yaɗa a shafukan sada zumunta sun nuna ɓaraguzan gidajen da aka rusa.

A ‘yan shekarun nan gwamnatin Kaduna ƙarƙashin jagorancin Nasir El-Rufai na rusa wurare da ta ce an gina su ba bisa ƙa’ida ba, ciki har daa kasuwanni.

160 COMMENTS

  1. Усик — Джошуа. Букмекери зробили прогноз на бій. Редкач аргументував такий сміливий прогноз тим, що попередні олімпійські чемпіони, яких побив Джошуа, були на заході кар’єри, тоді як Усик OleksandrUsyk “Зупинить за 5-7 раундів”: Зірковий супертяж зробив

  2. Промоутер Усика розповів про гонорар боксера за бій з Джошуа AnthonyJoshua Обсуждение:Энтони Джошуа — Александр Усик. Эта статья содержит текст, переведённый из статьи Anthony Joshua vs. Oleksandr Usyk из раздела Википедии на английском языке. Список авторов находится на

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...