Hajjin Bana: Maniyata a Kano sun fara karbar Kudinsu

Date:

Hukumar kula da jin dadin alhazai ta jihar Kano, ta fara dawowa da alhazan da suka yi niyyar gudanar da aikin Hajin shekarar 2021 kudadensu.

Da yake kaddamar da mika cakin kudin ga maniyyatan wanda aka gudanar a hedikwatar hukumar, Sakataren zartarwa na hukumar, Alhaji Muhammad Abba Danbatta, ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan hana zuwa aikin Hajjin bana da Hukumomin Masarautar Saudiyya suka yi

Danbatta ya yi nuni da cewa, bayan samun wannan bayani, Hukumar Aikin Hajji ta Kasa ta sanar da dukkan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha a hukumance.

Babban sakataren ya kara da cewa hukumar aikin hajji ta kasa ta gayyaci dukkan shugabannin hukumomin alhazai don ganawa da kuma mataki na gaba da ya kamata a dauka, wanda suka amince ba tare da wata tababa ba kan a biya maniyyatan kudadansu ko kuma a sanya su cikin shirin adashin gata ga wadanda suke da muradi

Sakataren zartarwar ya jaddada cewa sun fara aikin ne bayan samun izini daga Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a wannan batun, inda yay kira ga maniyyatan da su tuntubi Jami’an alhazai na kananan hukumominsu ko kuma duk wani jami’i a Hedikwatar kan mayar musu da kudaden nasu.

Dambatta ya tunatar da cewa, tuni Hukumar ta kaddamar da kwamitin mutum goma sha biyar wanda ya kunshi duka masu ruwa da tsaki da suka hada da, wadanda suka hada da na ‘yan sanda, hukumar tsaro ta farin kaya, Hukumar Shige da Fice ta Najeriya, da na hukumar karbar korafi ta jaha da kuma wakilin kafafen yada labarai da sauransu

Tun da farko, Shugaban Hukumar, Farfesa Abdallah Saleh Pakistan, ya shawarci Mahajjata da su dauki hana zuwa hajjin a matsayin nufin Allah Madaukakin Sarki da kuma ci gaba da yin addua ba dare ba rana domin Allah Ya kawar da annobar COVID-19 tare da samun zaman lafiya a Kano, Najeriya da ma duniya baki daya.

A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Mahajjatan da suka karbi cakin kudinsu, yabawa shugabancin Hukumar Alhazai ta Kano suka yi kan yadda suka tsara yadda za a mayar da kudaden.

305 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...