Gwamnonin PDP ba sa son a kawo karshen rikicin makiyaya – Buhari.

Date:

Fadar Shugaban Najeriya a ranar Laraba, ta zargi gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP, da kin goyon bayan kudirin kawo karshen rikicin makiyaya a kasar ta yadda za a ceci rayukan jama’a da dukiyoyinsu.

Fadar Shugaban kasar na bayyana hakan ne bayan taron da kungiyar Gwamnonin PDP ta gudanar a karshen mako a Uyo, jihar Akwa Ibom ranar Litinin.

A martaninta fadar shugaban kasar a cikin wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar a Abuja, ya ce gwamnonin PDP ba su samar da mafita ga matsalolin kasar ba amma sun fi sha’awar abin da ya shafe su .

A cewar sanarwar: “Wannan shirin na samar da matsuguni ga makiyaya ya kawo ‘yanci da sauyi na zamani don kawo mafita ga kalubalen da al’ummomi daban-daban na kasarmu suka fuskanta amma gwamnonin PDP suka ki amincewa da shi, suka hana dukkan’ yan Najeriya ‘yancinsu na tsarin mulki na rayuwa da aiki a kowace jiha ta Tarayya sun fi son yin kira ga rarrabuwar kawuna a tsakanin ‘yan Najeriya”

86 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...