Gwamnonin PDP ba sa son a kawo karshen rikicin makiyaya – Buhari.

Date:

Fadar Shugaban Najeriya a ranar Laraba, ta zargi gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP, da kin goyon bayan kudirin kawo karshen rikicin makiyaya a kasar ta yadda za a ceci rayukan jama’a da dukiyoyinsu.

Fadar Shugaban kasar na bayyana hakan ne bayan taron da kungiyar Gwamnonin PDP ta gudanar a karshen mako a Uyo, jihar Akwa Ibom ranar Litinin.

A martaninta fadar shugaban kasar a cikin wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar a Abuja, ya ce gwamnonin PDP ba su samar da mafita ga matsalolin kasar ba amma sun fi sha’awar abin da ya shafe su .

A cewar sanarwar: “Wannan shirin na samar da matsuguni ga makiyaya ya kawo ‘yanci da sauyi na zamani don kawo mafita ga kalubalen da al’ummomi daban-daban na kasarmu suka fuskanta amma gwamnonin PDP suka ki amincewa da shi, suka hana dukkan’ yan Najeriya ‘yancinsu na tsarin mulki na rayuwa da aiki a kowace jiha ta Tarayya sun fi son yin kira ga rarrabuwar kawuna a tsakanin ‘yan Najeriya”

86 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...

Al’ummar Garin Riruwai da wani Kamfanin Hakar ma’adanai Sun Cimma Yarjejeniya Kan Ci gaban yankin

Kwamitin ci gaban Al’ummar garajn Riruwai da wani kamfanin...