Duk lalacewar PDP gwara ita da jam’iyyar APC — Kwankwaso

Date:

 

Tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin mafi lalacewa cikin jam’iyyun siyasa a wannan lokaci, dukda dai yace itama PDP ba kanwar lasa bace wajen kama-karya a yanzu, domin duk cancantarka da haƙƙin ka, zaka iya rasa shi ta dalilin wasu sojojin gona.

Kadaura24 ta rawaito cewa, Kwankwaso ya bayyana haka ne jiya Lahadi, yayin taron masu ruwa da tsaki na Kwankwasiyya a gidansa dake Kano, inda yace har yanzu yana cikin jam’iyyar PDP, amma shirye-shirye sunyi nisa a tsakaninsa da jam’iyyar NNPP mai kayan marmari.

Kwankwaso yace fita daga jam’iyya da komawa ba illa bane, kuma hakan ma shi ne kwarewa a siyasa, domin a shekarar 2018 da sukayi zaben fidda gwani a Fatakwal, wadanda suka zo na farko, na biyu, na uku dana hudu, duk sunbar PDP sun dawo, sai kuma wasu tarkace da suka biyo baya, a cewar Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...