Gidauniyar Kashe kwabo dake Gwale ta yiwa yara 50 kaciya

Date:

Daga Ibrahim Abubakar Diso
Gidauniyar umar kashe kwabo dake Karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano ta yiwa yara hamsin kaciya tare da basu magani kyauta.
 an dai gudanar da wannan aiki ne a asibitin sha ka tafi dake Gwale kusa da ofishin hisba karkashin kulawar Sagir Ibrahim.
Shugaban gidauniyar Alh. Umar kashe kwabo yace yana daga cikin aikin wannan gidauniya tallafawa marasa karfi don ganin an fitar dasu daga cikin wani kangi.
Ya Kuma kara da cewa ko a ranar asabar din da ta gabata gidauniyar ta rabawa dalibai litattafai a unguwar Gwale tare da basu uniform kyauta, yace fatansu Allah ya fisu yaba wannan aiki da suke yi.
 Wasu da cikin iyayen yaran da akaiwa kaciyar sun godewa shugaban gidauniyar tare da  ina yin addu’ar o’ Allah ya dada bunkasa wannan gidauniya ta cigaba da tallawa marasa karfi.
Malam Sagir wanda yayi matukar nuna farin cikinsa dangane da kokarin da wannan gidauniya take yi, sannan ya ja hankalin masu hannu da shuni da suyi koyi da wannan gidauniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...