Wutar lantarki ta haddasa gobarar da ta gone kayan Sama da Miliyan 3 a Unguwar L/Makera dake kano

Date:

Daga Hussaini Kabir minjibir.

 

Gobara ta ƙone kaya da abinci da kuɗin su ya haura Naira miliyan uku da rabi a unguwar lokan maƙera ƙaramar hukumar Gwale dake birnin Kano.

Da yake jawabi ga manema labarai don gane da musababbin tashin gobarar, mai gidan malam sulaiman Abdullahi lokon makera ya bayyana cewa wutar ta tashi da misalin ƙarfe biyu na rana sakamakon wutar lantarki mai ƙarfi.

Inda yace wutar ta ƙone kayan sawa da kayan abinci da muhimman takardu da rufin ɗakuna guda huɗu.

Kadaura24 ta rawaito cewa ba a samu asarar rai ba kuma babu wanda ya sami rauni.

Tuni dai Hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban hukumar Dr. Sale Aliyu jilli ta ziyarci gidan da akai gobarar har kuma ta bashi gudunmawar kayan abinci da kayan rufin kwano da siminti da katifu domin rage masa raɗadi.

Ta kuma jajanta masa a madadin gwamnatin jihar Kano.

Ta kuma yi kira ga sauran al’umma da su dinga kiyaye wa da kayayyakin wuta musamman a wannan lokaci na hunturu.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...