Shirya taron zumunci zai wanzar da zaman lafiya a ƙasa – Ɗan kadan Kano

Date:

Daga. Nasiba Rabi’u Yusuf
Ɗan kadan Kano kuma Dan majen Gwandu Alhaji Bashir Ibrahim  Muhammad ya buƙaci al’umma da su riƙi zumunci a matsayin abinda zai ƙara kyautata alaƙarsu da yan uwan su a duk inda suke.
KADAURA24 ta rawaito Alhaji Bashir Ibrahim ya bayyana hakan a ranar Litinin, a wajen taron zuriyar Marigayi Moddibo Mahmud da kuma gabatar da littafin tarihin zuri’ar.
Ɗan kadan Kanon ya ce, kowacce zuri’a tana yin ƙarko ne a duk sanda ƴaƴan cikinta suka ɗauki matakan ingantata musamman ta hanyar shirya taruka.
“Muna sane da tarihin yadda kowacce zuriya ke fara da kaɗan, sai kuma ta bazu zuwa sassan duniya ta ci gaba da yaɗuwa ta hanyar hayayyafa”.
Zuri’ar Moddibo ta zo Kano ne tun daga zamanin marigayi sarki Abdullahi Maje Karofi ga shi a yanzu zuriyar ta fara tattaro kanta ta hanyar bincike da tuntuɓa”.
Alhaji Bashir Ibrahim ya kuma ce, ta hanyar shirya taron dangi ne za a san yawan zuri’a kuma zumunci zai ƙara danko da kuma samu haɗin kani da zaman lafiya.
Taron ya samu halartar ɗaukacin ƴaƴa da jikoki daga sassa daban daban na ƙasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...