Gwamnan Kano ya rabawa sabbin kwamishinonin da aka rantsar ma’aikatu

Date:

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir ya rantsar da Barr. Abdulkarim Kabir Maude a matsayin sabon kwamishinan Sharia kuma babban lauyan gwamnatin jihar Kano.

Kazalika gwamnan ya rantsar da Dr. Aliyu Isa Aliyu a matsayin Kwamishina a sabuwar ma’aikatar bunkasa al’amuran kiwon dabbobi.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma rantsar da Barr. Salisu Muhammad Tahir a matsayin babban sakatare a ma’aikatar Sharia ta jihar Kano.

Kotu Ta Dakatar da ‘Yan Sanda Daga Tilastawa Masu Motoci Mallakar Izinin Amfani da Gilashin Mota Mai Duhu

Da yake rantsar da sabbin kwamishinonin a yayin zaman majalisar zartaswa karo na 32, gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi kira garesu dasu zamo masu gaskiya da rikon amana a yayin gudanar da ayyukansu.

Ya ce nadin nadin nasu an yi shi ne bisa cancanta la’akari da gogewa da kwarewarsu da kuma irin gudummawar da suke bawa al’umar jihar Kano ta fannoni daban-daban.

Ya taya sabbin kwamishinonin murna tare da fatan zasu bada gudummawa wajen bunkasa cigaban jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Tinubu ya ba da Umarnin rage kudin aikin Hajjin 2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya umarci hukumar kula...

Hukumar yaƙi da cin-hanci ta jihar Kano ta fara binciken Ganduje kan zargin karkatar da Naira biliyan 4 a Kano

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da...

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics ta Yi Allah-wadai da Yunkurin Siyasantar da Bikin Cikar Najeriya Shekara 65 a Kano

Ƙungiyar Forum of Progressive Academics (FPA) ta yi Allah-wadai...

Yan Uwa da Abokan Arzikin Sabon Kwamishinan Shari’a na Kano Sun Shirya masa addu’o’i na musamman

Yan uwa da abokan arziki na kwamishinan shari'a na...