Karamar Hukumar Gwarzo ta amince da biyan kuɗin makarantar ɗalibai sama da Naira miliyan 31

Date:

Majalisar ƙaramar hukumar Gwarzo ta amince da ware sama da naira miliyan 31 domin biyan kuɗin makarantar ɗaliban da ke karatu a jami’o’i daban-daban a cikin gida da kuma ƙasashen waje.

Shugaban ƙaramar hukumar, Dakta Mani Tsoho, ne ya bayyana hakan lokacin da ya karɓi wakilan ƙungiyar ɗalibai mai suna Gida Gida Scholars a ofishinsa ranar Litinin.

Dakta Tsoho ya bayyana godiya ga Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, bisa wannan kyakkyawan shiri, inda ya roƙi ɗaliban su kasance jakadun jihar Kano na gari da kuma ƙaramar hukumar Gwarzo a duk inda suke karatu. Ya kuma tabbatar musu da cewa gwamnatin ƙaramar hukumar za ta ci gaba da tallafa musu don sauƙaƙa musu a harkokin karatunsu .

Za mu yi Aiki ba Dare ba Rana domin Tabbatar da Umarnin da Ganduje ya ba mu Baffa Babba Dan’agundi

A jawabin da shugaban ɗaliban ya gabatar a madadinsu, ya bayyana cewa ziyarar nasu ta kasance ne domin gode wa Gwamna Abba Kabir Yusuf, mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, da kuma shugaban ƙaramar hukumar Gwarzo, Dakta Mani Tsoho, bisa wannan tallafi mai muhimmanci. Ya kuma yi alkawarin cewa za su kasance wakilai nagari na jihar Kano a makarantunsu.

FB IMG 1753738820016
Talla

A wata sanarwa da jami’in yada labarai na shiyyar Gwarzo Auwalu Musa Yola ya a fitar , ya ce Shi ma sakataren ƙaramar hukumar Gwarzo, Alhaji Sunusi Abdullahi Getso, ya shawarci ɗaliban da su kasance jakadu nagari na Gwarzo da jihar Kano, tare da nisantar miyagun ƙungiyoyi da shaye-shaye.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...