Zargin cin zarafi: NAWOJ ta nemi Shugaban NRC ya baiwa tsohuwar Shugabar kungiyar Hakuri

Date:

Kungiyar ‘Yan Jarida Mata ta Najeriya (NAWOJ) ta yi tir da abin da ta kira cin zarafi da barazana ga tsohuwar shugabarta ta kasa, Comrade Ladi Bala, daga Daraktan Hukumar Sufurin Jirgin kasa ta Nigeria (NRC), Kayode Opeifa.

A cikin wata sanarwa da shugabar kungiyar ta kasa, Comrade Aisha Ibrahim, da sakatariyar ta kasa, Comrade Wasilah Ladan, suka rattaba wa hannu, kungiyar ta bukaci Daraktan ya fito fili ya bada hakuri ta hanyar wallafa sanarwar neman afuwa a jaridu fiye da guda daya, tare da yada shi a wata kafar rediyo ko talabijin.

FB IMG 1753738820016
Talla

NAWOJ ta kuma ce tun da cin zarafin ya shafi Hukumar Talabijin ta Kasa (NTA) inda Ladi Bala ke aiki, wajibi ne a kuma baiwa hukuma NTA hakuri .

Kungiyar ta bayyana cewa abin da ya faru barazana ce ga ‘yancin ‘yan jarida da tsaron su, lamarin da ta ce ba za ta lamunce shi ba.

NAWOJ ta zayyana bukatunta kamar haka:

Yin tir da cin zarafin da aka yi wa Ladi Bala wadda ta taba shugabantar kungiyar a matakin kasa.

Neman a bada hakuri a fili.

Daukar matakan da za su kare ‘yan jarida daga irin wannan cin zarafi a nan gaba.

Jaddada muhimmancin ‘yancin ‘yan jarida da tsaron lafiyarsu.

Kungiyar ta jaddada cewa kare lafiya da mutuncin ‘yan jarida shi ne babban abin da ya fi damunta, don haka ta bukaci Daraktan NRC ya gaggauta daukar matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...

NUC ta kakabawa jami’o’i takunkumi kan yadda suke ba da digirin girmamawa a Najeriya

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) ta sanar...