Kungiyoyin Kwaryar Bakin Kasuwa Sun Mika Godiya Ga Gwamna Abba

Date:

Gamayyar kungiyoyin ci gaban yankin Kwaryar Bakin Kasuwa sun mika sakon godiya da jinjina ga Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa amincewarsa da sanya fitilun titi a yankin — musamman a Zawiyar Sheikh Tijjani Usman Zangon Bare Bari.

Da dumi-dumi: Hadimin Gwamnan Kano ya maka mawallafin Jaridar Daily Nigerian Jafar Jafar a gaban Kotu

Kungiyoyin sun ce aikin ya zo a lokaci mai muhimmanci, ganin cewa ana shirye-shiryen gudanar da Mauludin Annabi (SAW) a zawiyar, inda fitilun za su taimaka wajen samar da haske da kuma inganta tsaro yayin taron.

FB IMG 1753738820016
Talla

Sun kuma bayyana farin cikinsu da yadda Gwamnan ya amince da bukatarsu cikin gaggawa da kulawa, abin da suka ce ya nuna irin yadda gwamnatinsa ke bai wa bukatun al’umma muhimmanci.

Kungiyoyin sun yi addu’ar Allah ya ci gaba da yi wa Gwamna jagora tare da ba shi ikon cigaba da irin wadannan ayyuka na alheri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...

NUC ta kakabawa jami’o’i takunkumi kan yadda suke ba da digirin girmamawa a Najeriya

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) ta sanar...