Gwamna Abba ya rantsar da sabon shugaban hukumar hana cin hanci da rashawa ta Kano

Date:

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya rantsar Alhaji Sa’idu Yahaya a matsayin sabon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano.

Da yake rantsar da sabon shugaban a gidan gwamnati, gwamna Abba Kabir Yusuf ya hore shi da ya zamo mai gaskiya da amana a yayin gudanar da aikinsa.

FB IMG 1753738820016
Talla

Yace gwamnati ta bashi wannan mukami ne la’akari da gudummawar da yake bayarwa wajen yaki da cin hanci da rashawa a jihar Kano da ma kasa baki daya.

Ya hore shi da ya zamo mai jajircewa da sadaukar da kai tare da tabbatar da adalci ga kowane bangare.

Magoya bayan NNPP Kwankwansiyya a Bagwai na neman agajin Gwamnan Kano da Dungurawa

Kazalika gwamna Abba Kabir Yusuf ya rantsar da karin masu bashi shawara na musamman da suka hadar da tsohon shugaban hukumar tallafin karatu ta jiha Alhaji Kabiru Haruna Ketso da Alhaji Sale Musa Sa’ad da kuma Sylvester Kole.

A nasa bangaren, sabon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jiha, Alhaji Sa’idu Yahaya ya yi alwashin gudanar da aikinsa bisa gaskiya da mana tare da yin aiki bisa tanadin doka domin tabbatar da kyakkyawan zaton da ake dashi a kansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...