Sarki Aminu Ado Bayero ya Mika Sakon Ta’aziyya ga Al’ummar Kasar Ghana

Date:

Daga Umar Ibrahim Usman

 

Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya mika ta’aziyya ga gwamnatin Ghana da iyalan wadanda rasuwar mutane takwas a hatsarin jirgin soja ta shafa a kasar.

A sakon da mai magana da yawunsa ya  Sarkin Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa Kadaura24 ya ce Sarkin ya bayyana wannan a matsayin babban rashi ga Ghana, Najeriya, da ma yankin Afirka ta Yamma baki ɗaya.

FB IMG 1753738820016
Talla

Ya mika sakon jaje da addu’a ga dangin mamatan da al’ummar Ghana, yana roƙon Allah Ya jikan su da rahama kuma Ya bai wa iyalan da ‘yanuwa haƙuri da juriya.

Gwamnan Kano ya Gabatarwa Majalisar Dokokin Jihar Wasu Manyan Bukatu

Idan dai ba a manta ba cikin mutanen takwas da su ka rasu a hadarin jirgin saman mai saukar ungulu akwai wasu ministoci biyu na tsaro Edward Omane Boamah da ministan muhalli Braham Murtala Muhammed da suka rigamu gidan gaskiya a hadarin na yankin Ashanti a daji da ke kusa da Obuasi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya Gabatarwa Majalisar Dokokin Jihar Wasu Manyan Bukatu

Daga Isa Ahmad Getso Majalisar dokokin jihar Kano ta karbi...

Sanya mata a shugabanci zai taimaka wajen kawo cigaba ga al’umma – NAWOJ Kano

Kungiyar mata ‘yan jarida ta Najeriya (NAWOJ), reshen jihar...

Gwamnan Kano ya raba tallafin kayan sana’o’i ga matasa 1130

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya raba tallafin...

‎2027: Tsohon SSG Na Kaduna Ya Shawarci Sha’ban Ya Bar APC Ya Shiga ADC Don Yin Takarar Gwamna

Daga Rahama Umar Kwaru ‎ ‎ ‎Wani bidiyo da ya fara yawo...