Yadda Wasu Matasa suka Kona Ofishin Sanata Barau Jibril

Date:

Wasu matasa sun ƙone wani ɓangare na ofishin sanata Barau Jibrin a Kano, jigo a ɓangaren APC da ya raba gari da ɓangaren gwamnan jihar.

Shaidu sun bayyanawa BBC cewar matasan sun fi 100 da suka abka wa ofishin jam’iyyar.

Wannan na zuwa a yayin da wata kotu a Abuja ta rushe shugabancin ɓangaren gwamna Ganduje tare da tabbatar da jagorancin ɓangaren Shekarau.

Rikicin siyasar APC a Kano na ci gaba da ɗaukar hankali a Najeriya tun bayan gudanar da zaɓen shugabannin jam’iyyar ɓangare biyu, inda wasu ke ganin rabuwar kai a Kano wata babbar ɓaraka ce ga APC.

Sai dai Rahotannin da Kadaura24 ta samu sun nuna Cewa tuni Jami’an Rundunar Yan Sanda Suka Isa wajen domin hana karya doka da Oda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...