Gwamnonin Nigeria na yunkurin dakatar da turawa kananan hukumomi kason kudadensu

Date:

 

 

Gwamnonin jihohin Nijeriya sun fara wani yunkuri na dakatar da shirin tura wa kananan hukumomin kasar kason kudaden su kai tsaye.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun tsaiko wajen aiwatar da hukuncin kotun koli kan ‘yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi.

InShot 20250309 102403344
Talla

Wasu daga cikin gwamnonin da suka gana da shugaban kasa Bola Tinubu a ranar Talatar makon jiya, sun yi watsi da matakin babban bankin Nijeriya CBN na tura kudin kai tsaye, inda suka bayyana cewa ana bin kananan hukumomin tulin bashi.

Yanzu-yanzu: EFCC ta bayyana dalilan da su ka sa ta kama Jarumar Tiktok Murja Kunya

Majiyoyin jaridar Punch a fadar shugaban kasa sun ce, gwamnonin sun nemi shugaban da ya sake duba kan lamarin.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a shekarar da ta gabata ne Kotun kolin Nigeria ta tabbatar da yankin cin gashin kan kananan hukumomi a Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira

Matatar Dangote ta sanar da dakatar da sayar da...

Neman Kudi na zo Kannywood ba fadakarwa ba – Sadiq Sani Sadiq

    Fitaccen jarumi a Masana’antar Kannywood Sadik Sani Sadik ya...

Hatsari Guda Biyu da Su ka Canza Rayuwar Matashi Nuraddin, Amma ba su Dakushe Burinsa ba

Nuraddin ya fuskanci manyan jarabawa guda biyu a rayuwar...

Zargin Handama: Al’ummar Garin Danzaki Sun Nemi Agajin Gwamnan Kano

Daga Rabi'u Usman   Al'ummar garin Danzaki sun koka da yadda...