Ganduje ya baiwa Waɗanda Gobarar Kasuwar Kurmi ta Shafa tallafin Naira Miliyan 2

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

 

Shugaban karamar hukumar birni da kewaye, Kwamared Faizu Alfindiki, ya damka Naira miliyan biyu ga ‘yan kasuwar kurmi ‘yan littattafai da ke layin Alhaji Matazu, wadanda gobara tai sanadiyar kone musu shaguna da kayayyaki.

Gwamnan Jahar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne yai umarnin bayarda kudin domin rage musu radadin abunda ya faru ta karkashin ma’aikatar kananan hukumomi wadda Hon. Murtala Sule Garo ke jagoranta.

 

Gobarar Kurmi: Fa’izu Alfindiki ya jajantawa yan Kasuwar da gobar ta shafa tare da basu damar Gina shagunansu

Shugaban karamar hukumar, a madadin gwamnatin jahar ya mika sakon jajantawa ga wadanda iftila’in gobara ta afkawa, sannan ya yi kira gare su da su yi hakuri, yana mai cewa gobarar jarrabawa ce daga Allah Madaukakin Sarki.

A jawabansu daban-daban Shugabani da ‘yan Kungiyar Masu sayar da littattafai a Kasuwar ta Kurmi sun yabawa gwamna Ganduje da Shugaban Karamar Hukumar Birni da kewaye Fa’izu Alfindiki bisa yadda Suka Nuna Damuwar su tun Daga Lokacin da iftila’in ya afku, tare da fatan Sauran Shugabani zasu yi koyi da su.

Kadaura24 ta rawaito a Ranar Litinin din data gabata ne kwamaret Fa’izu Alfindiki ya halasci Kasuwar domin jajanta musu tare da yin alkawarin Gwamnati zata tallafa musu domin rage musu radadin halin da Suka tsinci kansu a ciki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...