Gwamnatin Kano za ta gina dakunan karatu a kananan hukumomi 44

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada aniyar ta na samar da ingantattun dakunan karatu ga jama’a a fadin kananan hukumomin jihar 44 .

Mukaddashin sakataren hukumar kula da dakin karatu ta jihar Kano, Malam Suleiman Hodi Adamu ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai a ofishinsa.

Ya ce makasudin aikin shi ne farfado da dabi’ar karatu da bincike a tsakanin dalibai da masu bincike da nufin inganta tsarin koyo mai inganci.

Kotu Ta Rushe Kwamitin da Gwamnan Abba Kabir ya Kafa Don Bincikar Ganduje

Malam Adamu ya kara da cewa hukumar ta ziyarci karatu na kananan hukumomi 23, cikin 44 dake jihar.

A cewarsa, rangadin wani bangare ne na kokarin gwamnatin jihar na farfado da dakunan karatu da ake da su da kuma amfani da su domin ci gaban ilimi a jihar.

Talla

 

Mukaddashin sakataren zartarwa ya ce a karshen rangadin hukumar za ta mika rahoton ga ma’aikatar ilimi da nufin yin gyaran fuska kan yuwuwar samar da dakunan karatu a daukacin kananan hukumomi 44 na jihar.

“Gwamnatin Kano ta tallafa wa hukumarmu ta gudanar da rangadin duba dakunan karatu da muke da su a kananan hukumomi 23.

Rikicin Masarautar Kano: Alkali Ya Hana Lauyoyin Magana da Jaridu

“Mun je wurin ne da nufin farfado da su da kuma amfani da su, hakika wannan aikin zai farfado da dabi’ar karatu a tsakanin dalibanmu.

“Hakanan zai taimaka wa masu binciken mu wajen gudanar da bincike, sannan matasanmu za su koyi bincike.

“Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf a shirye take ta tallafa wa duk wani shiri da kuma ci gaban ilimi a jihar,” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...