Gwamnatin Kano ta baiwa yan sanda sabon umarni akan Sarki Aminu Ado Bayero

Date:

Gwamnatin Kano ta bayar da umarnin fitar da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero daga karamar fada ta Nassarawa da yake zaune a cikinta.

Gwamnatin ta bai wa kwamishinan ’yan sandan jihar wannan umarni tana mai cewa akwai kwaskwarima da za ta soma yi wa ginin fadar nan ba da jimawa ba.

Kwamishinan Shari’a kuma Lauyan Ƙoli na Jihar Kano, Barista Haruna Isa Dederi ne ya bayar da wannan sanarwar yayin wani taron manema labarai da ya gudana a yau Alhamis a Fadar Gwamnatin Kano.

Karin Haske Kan Hukuncin Kotu Game da Rikicin Sarautar Kano

Wannan dai na zuwa ne bayan hukuncin da wata Babbar Kotun Tarayya da ke jihar ta yanke a yau dangane da taƙaddamar Masarautar Kano.

Babbar Kotun Tarayyara ta ce dokar da ta rushe masarautu a jihar na nan daram amma kuma ta soke aiwatar da dokar wadda gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi.

A lokacin yanke hukuncin, Mai Shari’a Abdullahi Muhammad Liman ya ce ba daidai bane gwamnan jihar Kano ya aiwatar da dokar soke masarautun saboda akwai umurnin kotun da aka bayar da ya dakatar da duk wani yunkuri na gwamnan Kano wajen aiwatar da sabuwar dokar da ta cire rawanin sarakuna biyar a jihar ta Kano.

Mai shari’a Liman ya ce “A don haka na bayar da umurnin cewa dukkan matakan da gwamnati ta ɗauka na soke su amma hakan bai shafi sabuwar dokar masarautu ba. Amma sun shafi matakan da gwamna ya dauka ciki har da sanya hannu a sabuwar doka da kuma sake nada Sanusi.

Ya kamata Gwamnatin Kano ta Mutunta Umarnin Kotu – Dr. JY

Kotun ta ce “An soke dukkan matakan da masu kare kai a shari’ar suka ɗauka, amma kuma hakan bai shafi dokar ba.”

“Waɗanda ke kare kansu a shari’ar na sane da umurnin kotun duk da cewa ba a aika musu da kofin umurnin ba. Amma sun gani a kafafen soshiyal midiya, a don haka ba daidai bane su kawar da kai”, in ji Alkali Liman.

Mai shari’a Liman ya mayar da wannan ƙara zuwa wata Kotun Tarayyar karkashin mai shari’a Amobeda Simon amma har sai an kammala sauraren karar da ɓangaren gwamnati suka ɗaukaka.

Wannan al’amari na dambarwar masarautar Kano, tana ci gaba da ɗaukar hankali inda jama’a ke ci gaba da tofa albarkacin bakinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki

Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya...

Aiyuka 5 da Gwamnan Kano ya yi alkawarin yi, bayan dakatar da rusau a Rimin Zakara

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ziyarci garin Rimin Zakara...

Shugaban K/H Garun Mallam zai Raba Audugar Mata 500 ga Makarantun Sakandiren Matan yankin

Daga Safiyanu Dantala Jobawa Shugaban karamar hukumar garun mallam Aminu...

Inganta Noma: Sanata Barau zai tallafawa Matasa 558 daga Arewa maso yammacin Nigeria

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...