Wutar Lantarki Ta Kashe Barawon Taransufoma

Date:

Wutar lantarki ta kashe wani barawon tiransufoma a unguwar Jattu da ke Karamar Hukumar Etsako ta yamma a Jihar Edo.

Al’ummar unguwar dai sun wayi gari ne da ganin gawar barawon da ake zargi, tana lilo a jikin turakun wutar lantarki da ke hada da tiransfomar.
Sai da wanda ake zargin ya yanke wayoyin da ka karkashin tiransufomar, ya ajiye su a gefe, sannan ya hau sama zai yanko dogayen wayoyin da ke raba wutar, inda a nan ne ya gamu da ajalinsa.
Shaidu sun bayyana cewa daga bisani jami’an Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Edo (BEDC) sun zo sun dauke gawar suka tafi da ita.
Kakakin ’yan sandan jihar, SP Chidi Nwabuzor, dai ya ce ba shi da labarin abin da ya faru.
Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...