Yanzu-yanzu Kotun Ƙoli Ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaɓen Gwamnan Adamawa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kotun koli ta tabbatar da zaben gwamna Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan jihar Adamawa.

Kadaura24 ta rawaito mai shari’a John Okoro wanda ya karanta hukuncin a ranar Laraba, ya yi watsi da karar da ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar APC, Aisha Dahiru ta shigar.

Yadda Aka Shawo Kan Likitocin Asibitin Murtala dake Kano Suka Koma Bakin Aiki

A yayin da ya yi watsi da karar da ta shigar bisa rashin cancantar ta, alƙalan biyar karkashin jagorancin Mai Shari’a John Okoro sun bayyana cewa, abin da Kwamishinan Zabe (REC), Hudu Ari ya aikata rashin gaskiya ne kuma ya aikata laifuka babba.

Sabon Gwamnan Kogi Ya Zo da Sabon Salo a Dimokaradiyyar Nigeria

Mai shari’a Okoro ya kara da cewa, jami’in tattara sakamakon zabe shi ne ya cancanta ya fadi sakamakon ba Ari ba.

Ya bayyana cewa dokar zabe ta dora alhakin bayyana sakamakon zabe akan wanda aka nada a matsayin jami’in tattara sakamakon zaben, kuma wannan jami’i shi ka dai ne ke da ita ba wani ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Kawu Sumaila ya jinjinawa Gwamnan Kano

Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar...

Gwamna Yusuf Ya Shirya Baiwa Kananan Hukumomin Kano Cikakken ‘Yan cin Kai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Majalisar Zartarwa ta jihar Kano ta Amince da kashe Naira Biliyan 18 don aiwatar da wasu aiyuka

  Majalisar zartarwar jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir...

Gwamnatin Kano ta nemi majalisar dokokin jihar ta haramta auren jinsi

Gwamnatin jihar Kano ta buƙaci majalisar dokokin jihar ta...