Yanzu-yanzu Kotun Ƙoli Ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaɓen Gwamnan Adamawa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kotun koli ta tabbatar da zaben gwamna Ahmadu Fintiri a matsayin gwamnan jihar Adamawa.

Kadaura24 ta rawaito mai shari’a John Okoro wanda ya karanta hukuncin a ranar Laraba, ya yi watsi da karar da ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar APC, Aisha Dahiru ta shigar.

Yadda Aka Shawo Kan Likitocin Asibitin Murtala dake Kano Suka Koma Bakin Aiki

A yayin da ya yi watsi da karar da ta shigar bisa rashin cancantar ta, alƙalan biyar karkashin jagorancin Mai Shari’a John Okoro sun bayyana cewa, abin da Kwamishinan Zabe (REC), Hudu Ari ya aikata rashin gaskiya ne kuma ya aikata laifuka babba.

Sabon Gwamnan Kogi Ya Zo da Sabon Salo a Dimokaradiyyar Nigeria

Mai shari’a Okoro ya kara da cewa, jami’in tattara sakamakon zabe shi ne ya cancanta ya fadi sakamakon ba Ari ba.

Ya bayyana cewa dokar zabe ta dora alhakin bayyana sakamakon zabe akan wanda aka nada a matsayin jami’in tattara sakamakon zaben, kuma wannan jami’i shi ka dai ne ke da ita ba wani ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...