Yadda Nigeria ke samun Cigaba a Yaki da Cin Hanci da Rashawa – CISLAC

Date:

Wata kididdiga da kungiyar Transparency International ta fitar kan rashawa ta nuna cewa an samu ci gaba wajen yaki da matsalar a Najeriya inda a yanzu kasar ke mataki na 145 cikin kasashe 180 da aka yi nazari a kai.

Kididdigar ta nuna cewa Najeriya ta kara maki daya kan maki 24 da take da shi a baya inda a yanzu take da maki 25 cikin 100 baya ga matsawa daga matsayinta na 150.

Kotun Ƙoli: Shin da gaske ne an kwalla yarjejeniya tsakanin Gwamnan Kano da Tinubu ?

Kididdigar na duba yadda yanayin matsalar rashawa take a gwamnatin kasashen da aka yi nazari akan su.

Tana bai wa kowace kasa maki daga 0 zuwa 100 – 0 na nufin matsalar rashawa ta yi katutu yayin da 100 ke nufin nasara a yaki da rashawa.

Sabon Gwamnan Kogi Ya Zo da Sabon Salo a Dimokaradiyyar Nigeria

Cibiyar Rajin Kyautata Ayyukan Majalisun Dokoki da Yaƙi da Rashawa a Najeriya CISLAC wadda ta gabatar da jadawalin a Abuja, ta ce makin da Najeriya ta samu kasa yake da maki 33 na kasashen da ke kudu da hamadar sahara.

Jadawalin bai fito da bayanan rashawa ba a kasar amma ya bayyana yadda ake kallon cin hanci a Najeriya.

Cislac ta ce kididdigar ba wai tana nazarin ayyukan hukumomin yaki da rashawa ba ne da ta ce suna kokari wajen yakar cin hanci a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...