Yadda Nigeria ke samun Cigaba a Yaki da Cin Hanci da Rashawa – CISLAC

Date:

Wata kididdiga da kungiyar Transparency International ta fitar kan rashawa ta nuna cewa an samu ci gaba wajen yaki da matsalar a Najeriya inda a yanzu kasar ke mataki na 145 cikin kasashe 180 da aka yi nazari a kai.

Kididdigar ta nuna cewa Najeriya ta kara maki daya kan maki 24 da take da shi a baya inda a yanzu take da maki 25 cikin 100 baya ga matsawa daga matsayinta na 150.

Kotun Ƙoli: Shin da gaske ne an kwalla yarjejeniya tsakanin Gwamnan Kano da Tinubu ?

Kididdigar na duba yadda yanayin matsalar rashawa take a gwamnatin kasashen da aka yi nazari akan su.

Tana bai wa kowace kasa maki daga 0 zuwa 100 – 0 na nufin matsalar rashawa ta yi katutu yayin da 100 ke nufin nasara a yaki da rashawa.

Sabon Gwamnan Kogi Ya Zo da Sabon Salo a Dimokaradiyyar Nigeria

Cibiyar Rajin Kyautata Ayyukan Majalisun Dokoki da Yaƙi da Rashawa a Najeriya CISLAC wadda ta gabatar da jadawalin a Abuja, ta ce makin da Najeriya ta samu kasa yake da maki 33 na kasashen da ke kudu da hamadar sahara.

Jadawalin bai fito da bayanan rashawa ba a kasar amma ya bayyana yadda ake kallon cin hanci a Najeriya.

Cislac ta ce kididdigar ba wai tana nazarin ayyukan hukumomin yaki da rashawa ba ne da ta ce suna kokari wajen yakar cin hanci a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Kawu Sumaila ya jinjinawa Gwamnan Kano

Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar...

Gwamna Yusuf Ya Shirya Baiwa Kananan Hukumomin Kano Cikakken ‘Yan cin Kai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Majalisar Zartarwa ta jihar Kano ta Amince da kashe Naira Biliyan 18 don aiwatar da wasu aiyuka

  Majalisar zartarwar jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir...

Gwamnatin Kano ta nemi majalisar dokokin jihar ta haramta auren jinsi

Gwamnatin jihar Kano ta buƙaci majalisar dokokin jihar ta...