Daga Aisha Aliyu Umar
Gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin masu bashi shawara na musamman har guda 10 , a wani ɓangare na cika alkawuran da yayi yakin neman zabe.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Wadanda aka nadan sun hadar da:
1. Hon. Garba Dirbunde, mai ba da shawara na musamman kan harkokin kananan hukumomi
2. Hon. Wakili Aliyu Garko, mai ba da shawara na musamman kan harkokin kasashen waje
3. Air Commodore Yusha’u Salisu Tudunwada Wada, Rtd. Mai ba da shawara na musamman, akan harkar Tsaro.
4. Hon. Musa Ado Tsamiya, mai ba da shawara na musamman, kan Magudanan ruwa

5. Gwani Musa Falaki, mai ba da shawara na musamman kan harkokin addini II
6. Dr. Sulaiman Wali Sani, mai ba da shawara na musamman kan harkokin ma’aikatan gwamnati.
7. Farfesa Auwalu Arzai, mai ba da shawara na musamman kan ilimi mai zurfi.
8. Hon. Ahmad Sawaba, mai ba da shawara na musamman kan kula da namun daji.
9. Alh. Tajuddeen Gambo, mai ba da shawara na musamman kan ilimi.
10. Hon. Baba Abubakar Umar, mai ba da shawara na musamman na makarantu masu zaman kansu da na sa kai.
Gwamanan yace an nadasu ne bisa cancanta, aminci da jajircewa wajen yiwa mutanen jihar Kano hidima.
Sanarwar tace nadin nasu ayi shi ne bisa chanchanta sadaukar da kai da kuma la’akari da irin gudunmawar da suka bayar yayin zabe.