Ku daina yiwa Masu kudin cikin ku hassada – Sheikh Abdulwahab Abdullah ya fadawa talakawa

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Babban malamin addinin musuluncin nan dake Kano Sheikh Abdulwahab Abdullah ya bukaci talakawa da su guji yiwa mawadaka hassada akan arzikin da Allah ya yi musu.

 

” Masu kudi ya kamata ku rika bada zakka tare da tallafawa masu karamin karfi saboda tana magance hassada da kiyayya tsakanin mawadata da mabukata”.

Bankwana: Gwamna Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano

Sheikh Abdulwahab Abdullah ya bayyana hakan ne yayin da hukumar zakka ta jihar kano ta rabawa mabukata zakkar bana a gidan gwamnatin jihar kano.

 

Malamin ya kuma ce bai kamata talakawa su rika yiwa Masu kudi hassada ba saboda Allah ne ya basu, sannan ya bukace su da su rika godewa masu basu zakka da tallafa musu kamar yadda Annabi S A W yayi umarni.

 

Ya godewa Alh. Aminu Dantata bisa zakkar Naira Miliyan 10 da ya domin rabawa ga mabukata a jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...

Zargin kwace gona: Majalisar Dokokin Kano zata binciki Shugabar Karamar Hukumar Tudun Wada (ALGON)

    Majalisar dokokin jihar Kano, ta sha alwashin gudanar da...

Tinubu ya yi wa Buhari abun da Buharin ya kasa yi wa kakana- Jikan Shagari

Daga Nasiba Rabi'u Yusuf   Nura Muhammad Mahe, jikan tsohon shugaban...

Yanzu-yanzu: Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya fice daga...