INEC ta fara karɓar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da jihar Ekiti

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Jihar Ekiti da ke kudu mao yammacin Najeriya ta kasance jiha ta farko da ta fara gabatar da sakamakonta na zaben shugaban ƙasar da aka gudana ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu.

Shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmood ya bayar da dama ga babban jami’in haɗa sakamakon zabe a jihar ta Ekiti domin gabatar da sakamakon a zauren tattara sakamakon dake Abuja

Babban jami’in lura da zaben jihar ta Ekitin ne ya jagoranci gabatar da sakamakon kamar haka:

APC – 201,494

PDP – 89,554

LP – 11,397

NNPP – 264

SDP – 2011

Sakamakon ya nuna cewa jami’iyyar APC ce ta samu nasara a zaɓen na jihar Ekiti.

Sai dai babban jami’in hada sakamakon zaɓen ya ce an soke zabe a wasu mazaɓu biyu saboda wasu matsaloli guda biyu da suka hadar da:

Tangardar na’urar BVAS

Da kuma samun adadin mutanen da suka kada kuri’a a mazabar ya zarta adadin mutanen da na’uar BVAS ta tantance

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu Yanzu: Hukumar KNUPDA ta rushe gaban shagon jarumar Tiktok Rahama

Daga Rahama Umar Kwaru   Hukumar KNUPDA ta kaddamar da rushe...

Wata kungiya ta bukaci Gwamnan Kano ya dakatar da Shugaban karamar hukumar Gwale

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Wata kungiya mai zaman kanta mai...

Kwankwaso ba zai koma APC ba – Buba Galadima

Kusa a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya karyata jita-jitar...

Yadda gwamnan Kano ya ke rabon kujerun aikin hajjin bana kamar gyada

Daga Rahama Umar Kwaru Al'ummar jihar Kano na cigaba da...