Kano: Ma’aikatar Mata ta yaba wa NAWOJ kan shirye-shiryen wayar da kan mata

Date:

Ma’aikatar Harkokin Mata, Yara da Mutanen da ke da Bukatu na Musamman ta Jihar Kano ta jinjinawa ƙungiyar ’Yan Jarida Mata ta Najeriya (NAWOJ), reshen jihar Kano, bisa jajircewarsu wajen inganta lafiyar mata, ƙarfafa su, da kuma wayar da kan al’umma.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa Mai dauke da sa hannun shugabar kungiyar Bahijja Malam Kabara da mataimakiyarta Aisha Muhd Yanleman, kuma aka aikowa Kadaura24.

Sanarwar ta ce Kwamishinar ma’aikatar, Hajiya Amina Abdullahi Hod, wacce Hajiya Nafi Muhammad Yakasai ta wakilta, ce ta yaba wa NAWOJ bisa shirye-shiryen da suke gudanarwa, musamman taron bita da wayar da kai ga manbobinsu kan cutar sankarar mama.

InShot 20250309 102512486

Haka kuma, ta mika godiya ga gidauniyar Aminu Magashi Foundation (AMG) bisa daukar nauyin taron wayar da kan Sankara mama da goyon bayan shirye-shiryen kula da lafiyar mata a faɗin jihar. Ta ce tallafin da gidauniyar ke bayarwa yana taimakawa sosai wajen ƙara kusantar da bayanan lafiya ga mata .

NURTW ta Karrama DMD Karota Auwal Aranposu

Hajiya Nafi ta kuma yi godewa Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa goyon bayansa ga al’amuran da suka shafi mata, yara, da masu buƙatu na musamman.

A nata bangaren, Shugabar kungiyar NAWOJ ta jihar Kano, Comrade Bahijja Malam Kabara, ta gode wa Ma’aikatar Mata bisa hadin kan da take baiwa kungiyar da kuma yadda take tallafawa mata da kananan yara a kano.

Ta tabbatar da cewa NAWOJ za ta ci gaba da gudanar da ayyukan wayar da kai kan matsalolin da suka shafi mata tare da hada kai da gwamnati, kungiyoyi masu zaman kansu domin inganta rayuwar mata da yara a Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NURTW ta Karrama DMD Karota Auwal Aranposu

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababa hawa ta jihar...

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...