NUC ta kakabawa jami’o’i takunkumi kan yadda suke ba da digirin girmamawa a Najeriya

Date:

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Ƙasa (NUC) ta sanar da sabbin matakai domin dakile yadda ake ba da digirin girmamawa ba bisa ka’ida ba, ciki har da haramta bai wa duk wani jami’in gwamnati mai rike da mukami irin wannan digiri.

Shugaban Hukumar NUC, Farfesa Abdullahi Yusufu Ribadu, ne ya bayyana haka a Abuja ranar Juma’a yayin da ya karɓi rahoton kwamitin da aka dorawa alhakin binciken yadda ake bayar da digirin girmamawa da kuma yadda masu karɓa ke amfani da su .

InShot 20250309 102512486

Farfesa Ribadu ya ce hukumar ta shiga lamarin ne bayan binciken da aka gudanar a fadin ƙasa kan hanyoyin da ake bi wajen bayar da digirin girmamawa da yadda ake amfani da shi.

“An samar da waɗannan digirgir ne domin karrama mutanen da suka yi abin a-zo-a-gani, amma abin bakin ciki shi ne yadda aka fara karkatar da manufar zuwa wani abun na daban,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa matsalar ta ta’azzara sakamakon yawaitar makarantu na bogi da waɗanda hukumomi na cikin gida da na waje ba su aminta da su ba kuma suka mayar da digirin girmamawa tamkar kasuwanci.

Solacebase

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...

Tsoffin Kwamishinonin Kano sun Musanta labarin goyon bayan Sanata Barau a 2027

Kungiya ta tsoffin kwamishinoni da suka yi aiki a...

Kungiyar Iyayen Daliban MAAUN Ta Karyata Koken da Aka Kai wa PCACC, Ta Ce Jami’ar Na Da ‘Yancin Kanta

Shugaban Kungiyar Iyayen daliban  jami’ar MAAUN, Alhaji Mustapha Balarabe,...