Gwamnatin Kano ta baiyana lokacin da za ta kammala aikin gadojin sama na Tal’udu da Dan’Agundi — Kwamishina

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada aniyarta na kammala manyan ayyukan gine-gine da nufin inganta walwalar jama’a.

Kwamishinan Sashen Kula da Ayyuka, Nura Ma’aji, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Kano ranar Talata, bayan duba wasu ayyukan da ake ci gaba da gudanarwa a fadin jihar.

A cewar sa, aikin gina gadar sama ta Dan’Agundi da ta Tal’udu zai kammalu kafin karshen watan Disamba.

Ma’aji ya ce an riga an biya diyya da warware duk wasu batutuwan da suka shafi aikin domin tabbatar da kammalawarsa a kan lokaci.

Ya bayyana cewa ana gudanar da binciken aiki a kai a kai domin tabbatar da inganci da saurin ci gaba, tare da jaddada cewa wadannan gadaje za su taimaka wajen rage cunkoson ababen hawa a birnin Kano.

Kwamishinan ya kara da cewa an tsara kaddamar da ayyukan a watan Janairu 2026 a matsayin wani bangare na shirin gwamnatin jihar na ci gaban kayayyakin more rayuwa.

Ya bukaci goyon bayan jama’a domin ganin an cimma manufofin gwamnati yadda ya kamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kashim Shattima ya sauka daga kujerar ta mataimakin shugaban Nigeria ya baiwa wata yarinya

Mataimakin shugaban Kasa Kashim Shattima ya sauka daga kujerarsa...

Za a sanya Maiwushirya da Ƴar Guda cikin shirin auren gata – Hisbah

  Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta yaba da hukuncin...

RMK@69: Tinubu ya yi wa Kwankwaso kyakykyawan yabo

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika sakon taya...

NAHCON ta kafa kwamitin sa ido kan harkokin jiragen sama domin aikin Hajjin 2026

Shugaban Hukumar Kula da Alhazai ta Kasa (NAHCON), Farfesa...