An Fara Binciken Wani Tsohon Gwamna Kan Zargin Daukar Nauyin Yiwa Tinubu Juyin Mulki

Date:

Rahotanni sun bayyana cewa ana binciken wani tsohon gwamna daga ɗaya daga cikin jihohin kudancin Najeriya bisa zargin alaƙa da wasu jami’an soji 16 da aka kama bisa zargin shirya juyin mulki.

Majiyoyi sun tabbatar wa da jaridar Daily Trust cewa tsohon gwamnan na iya zama ɗaya daga cikin masu tallafawa shirin da aka ce an tsara aiwatar da shi a ranar 25 ga Oktoba.

An ce jami’an da ake tsare da su, ciki har da Brigadier Janar da Kanal, suna aiki a Ofishin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Ƙasa.

Hukumar leken asiri ta tsaro (DIA) ce ke jagorantar binciken, tare da wakilai daga rundunonin soji uku. Majiyoyi sun bayyana cewa tsohon gwamnan yana da tarihi a harkar man fetur da iskar gas, kuma ana iya gayyatarsa idan aka tabbatar da hujjar haɗin kai tsakaninsa da jami’an da ake tsare da su.

 

Sai dai Hedkwatar Tsaron Ƙasa (DHQ) ta karyata labarin cewa akwai yunƙurin juyin mulki, tana mai cewa jami’an da aka kama ana bincikensu ne kan rashin ladabi da karya ƙa’idar aiki, ba wani shirin kifar da gwamnati ba.

 

Shelkwatar tsaron ta jaddada cewa rundunar sojojin Najeriya tana nan daram wajen biyayya ga kundin tsarin mulki da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, tana kuma roƙon jama’a da su ƙaurace wa yada jita-jita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kashim Shattima ya sauka daga kujerar ta mataimakin shugaban Nigeria ya baiwa wata yarinya

Mataimakin shugaban Kasa Kashim Shattima ya sauka daga kujerarsa...

Gwamnatin Kano ta baiyana lokacin da za ta kammala aikin gadojin sama na Tal’udu da Dan’Agundi — Kwamishina

Gwamnatin Jihar Kano ta sake jaddada aniyarta na kammala...

Za a sanya Maiwushirya da Ƴar Guda cikin shirin auren gata – Hisbah

  Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta yaba da hukuncin...

RMK@69: Tinubu ya yi wa Kwankwaso kyakykyawan yabo

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika sakon taya...