Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Date:

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin jagorancin Mai Shari’a Josephine Obanor, ta tabbatar da cewa Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) na da cikakken ikon gudanar da bincike kan yadda ake tafiyar da kuɗaɗen tallafin karatu na jihar Kano.

Majiyar Kadaura24 ta Solacebase ta ce Rahoton ya bayyana cewa, ICPC ta gayyaci jami’an Ma’aikatar Ilimi mai zurfi ta jihar Kano dana hukumar tallafin karatu domin su kawo wasu takardu da kuma bayyana wasu bayanai da ake bincike a kansu.

Sai dai, babban sakataren ma’aikatar, Dr. Hadi Bala, tare da wasu jami’an, sun shigar da ƙara a kotu suna masu neman kotun ta hana binciken domin yin binciken ko gayyyararsu tauye musu ’yancin su ne na dan Adam.

Da fari dai ita hukumar ICPC korafi ta samu game da zargin wata almundahana da aka ce an yi a hukumar lamarin da ya sanya ta fara bincike, Wanda hakan yasa aka kata kara Kotu.

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Yayin yanke hukuncin Kotun ta yi watsi da wannan ƙara, inda ta bayyana cewa:

1. Gayyatar ICPC ba take hakkin kowa ba – Domin kawai neman takardu ko bayanai don bincike ba ya nufin tauye ’yancin ɗan adam.

2. Kotun ta ce shigar da Babban lauyan Kasa shi cikin ƙarar bai da amfani.

3. Kotun ta jaddada cewa hukumar ICPC tana da ikon gudanar da cikakken bincike kan duk wani zargin almundahana da kudaden gwamnati.

FB IMG 1753738820016
Talla

Wannan hukunci ya sake tabbatar da cewa babu wanda ya fi karfin doka, kuma an bai wa ICPC ƙarfin iko wajen tabbatar da gaskiya da ingantaccen amfani da kuɗaɗen jama’a, musamman kuɗin da aka ware domin tallafawa ɗalibai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...