Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Date:

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar da sakamakon jarrabawar wannan shekara ta 2025.

Sakamakon ya nuna cewa kashi 60.26 cikin 100 na waɗanda suka samu kiredita biyar zuwa sama ciki har da darussan Lissafi da Turanci.

FB IMG 1753738820016
Talla

Shugaban hukumar Farfesa Ibrahim Wishishi ya shaida wa BBC cewa jihar Kano ce kan gaba a yawan ɗaliban da suka samu nasara a jarrabawar a faɗin wuraren da hukumar ke shirya jarrabawar da suka haɗa da wasu ƙasashen Afirka.

Cikin wata sanarwa da gwamnatin Kanon ta fitar ta ce wannan ne karon farko cikin shekara 25 da jihar ta samu wannan nasara.

 

Shugaban na NECO ya ce cikin ɗalibai 1,358,339 da suka rubuta jarrabawar, yayin da 818,492 ne suka samu kiredit a darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Karamci United Family ta Karrama Shugaban gidan Radiyon Pyramid Saboda Taimakawa Al’umma

Shugaban gidan Radio tarayya Pyramid FM Dr. Garba Ubale...

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...