Dalilan Hukumar tace fina-finai ta Kano na haramta muƙabalar tsakanin masu waƙoƙin yabon Ma’aiki S A W

Date:

Hukumar Tace Fina-finan Jihar Kano ta sanar da haramta dukkan muƙabalar mawakan addini a jihar, sai dai idan an samu sahalewar hukumar tun kafin gudanar da su.

Shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin kaddamar da kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Malam Isha Abdullahi, Daraktan Harkokin Musamman na hukumar.

El-Mustapha ya ce an ɗauki wannan mataki ne sakamakon muƙabalar da aka gudanar ba tare da izini ba tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi, wadda ya bayyana a matsayin karya ƙa’idodin hukumar.

Hukumar ta bai wa mawakan biyu tare da masu gabatar da muƙabalar wa’adin awanni 24 su bayyana gaban kwamitin binciken.

FB IMG 1753738820016
Talla

A cewar hukumar, shirya irin wannan muƙabala ba tare da amincewar ta ba ya sabawa dokar Tace Fina-finan Jihar Kano, kuma hakan na iya haifar da ɗaukar matakan shari’a masu tsanani.

Shugaban hukumar ya jaddada kudirin hukumar na ci gaba da tsarawa da kuma sa ido kan harkokin mawakan addini da masu nishadantarwa a jihar, bisa tanadin doka. Ya kuma yi kira ga al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da tallafa wa hukumar da bayanai masu amfani da za su kawo zaman lafiya, fahimtar juna, da bunƙasar al’adu a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke hukunci kan ko ICPC tana da ikon gudanar da binciken kudin tallafin karatu na Kano

Babbar Kotun tarayya dake Babban Birnin Tarayya (FCT), karkashin...

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...