Al’ummar Danbare, Hawan Dawaki da Makwabtansu Sun Koka Kan Yunkurin Kwace Filin Makaranta

Date:

Al’ummomin unguwannin Danbare, Hawan Dawaki, Kuyan Ta Inna, Gwazaye da Yammawa sun yi kira ga hukumomi da su kawo dauki cikin gaggawa kan yunkurin da wasu mutane ke yi na kwace filin makarantar gwamnati a yankin Kuyan Ta Inna.

Mutanen yankin sun bayyana damuwarsu ne bayan da wasu suka fara gina gine-gine a kan wasu filaye da aka ware tun da farko domin asibiti da masallaci, sannan suka karkata hankalinsu zuwa filin makaranta.

FB IMG 1753738820016
Talla

A cewar mazauna yankin, hakan barazana ce ga makomar ilimi da cigaban al’ummar yankin.

Shugaban kwamitin ci gaban yankin, Baba Habu Miika’ilu Warure, ya ce wannan lamarin ya haifar da fargaba mai tsanani a tsakanin iyaye da yara, domin rashin makaranta a yankin zai jefa su cikin babban kalubale.

Da yake karin bayani, shugaban karamar hukumar Kumbotso, Hon. Abdullahi Ghali Basaf, ya tabbatar da cewa sun karbi korafin jama’a, kuma tuni an dauki matakan dakile yunkurin kwace filin.

“Muna da niyyar gina makaranta a filin domin kare hakkokin al’umma. Ba za mu lamunci duk wani yunkuri na kwace filayen da aka ware musu ba,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...