Gwamnatin taraiya ta baiwa dalibar da ta lashe gasar Ingilishi ta duniya kyautar Naira dubu 200

Date:

A yau Alhamis, Gwamnatin Tarayya ta baiwa Nafisah Abdullahi, wadda ta lashe gasar TeenEagle Global Finals, kyautar N200,000.

Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ne ya mika wannan lambar yabo a wani biki da aka gudanar a Abuja.

FB IMG 1753738820016
Talla

A baya-bayan nan, Atiku Foundation ta baiwa zakarun gasar TeenEagle — Nafisa Abdullahi, Rukaiya Fema da Khadija Kalli — guraben karatu da aka dauki nauyinsu saboda bajintar da suka nuna a gasar TeenEagle Global Finals.

Da dumi-dumi: Farfesa ya Zama Sakataren Ilimi na karamar Hukuma a Kano

Wadannan ‘yan mata, wadanda suka fito a matsayin zakarun duniya a fannoni daban-daban na gasar, sun samu yabo daga gudauniyar saboda abin da ta kira “nasara mai ban mamaki.”

Daga cikin wadanda suka samu wannan yabo akwai Nafisa Abdullahi ‘yar shekara 17, wadda ta fito fili saboda kwarewarta a harshen Ingilishi, tunani mai zurfi da kuma iya bayyana magana, abubuwan da suka taimaka mata wajen doke mahalarta daga kasashe 69.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...