Da dumi-dumi: Sanarwa ta Musamman daga Gwamnatin jihar Kano

Date:

Assalamu Alaikum.

Sanarwa ta musamman!

Gwamnatin jihar Kano na gargaɗi kan waɗanda ɓata garin matasa ke siyarwa da Rodika na slap, ƙarafunan futulun kan titi da wayoyin lantarki na gwamnati idan sun sace a kan tituna.

Mai girma gwamna Alhaji Abba K Yusuf, ya bada umarni na musamman ga ma’aikatar ayyuka ta jihar Kano, an janyo shugabannin masu harkar ƙarafuna na jihar Kano ana zaman tattaunawa da su dangane da matsalolin da suke faruwa musamman a kan sana’arsu, kwamitin ya haɗa da jami’an tsaro da sauransu.

“Idan har masu sana’ar ba sa siyan waɗancan kayayyaki na gwamnati to fa ba za su dinga zuwa su na sacewa ba, domin da yawan guraren da suke zuwa su farfashe slap ko wayoyin gwamnati da ƙarafuna ba ma aiki ne ya biyo ta wajen ba.

“Duk wanda aka riƙe ba zai ji da daɗi ba, yanzu daga ɓata garin matasan har waɗanda suke kawowa su siya an kafa tsatstsauran kwamiti wallahi duk wanda aka kama ba zai ji da daɗi ba!”.

 

“Iyaye, shugabannin unguwa da masu faɗa a ji su ja kunnen yayansu, yan kasuwa su guji siyan kayan da suka tabbatar daga hannun bata gari ya fito ko dukiyar gwamnati.

FB IMG 1753738820016
Talla

“Yanzu da wanda ya sato da wanda ya siya duk sunansu daya ne! “Barayi! Idan su ka kama mutum ba zai ji da daɗi ba!

Allah ya cigaba da daga martabar jihar Kano. Amin.

Engr. Marwan Ahmed
Hon. Commissioner
Ministry Of Works, Kano State.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Karamin Minista Yusuf Ata ya mayarwa da Abdullahi Abbas Martani

Karamin Ministan Ma’aikatar Gidaje da Bunƙasa Birane na tarayyar...

APCn Kano ta Kai karar Minista Yusuf Ata wajen Shugaban Kasa Tinubu

Jam’iyyar APC a Kano ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya Abdullahi...

‎Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya ‎

‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun kwana...