Nan gaba kadan za mu bayyana sunayen masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya – Babban Hafsan tsaro

Date:

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce nan ba da jimawa ba za a bayyana sunayen masu daukar nauyin ta’addanci a ƙasar tare da gurfanar da su a gaban shari’a.

Ya bayyana hakan ne a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels , inda ya ce jinkirin ya samo asali ne daga rikice-rikicen shari’a da kuma alakar wasu daga cikin kuɗaɗen da ake amfani da su wajen daukar nauyin ta’addanci da ƙasashen waje.

FB IMG 1753738820016
Talla

Musa ya ce an gano wasu daga cikin masu daukar nauyin suna cikin ƙasar, inda sukan ɗauki matasa aiki, su ba su babura, sannan su rika tura kuɗaɗe zuwa wasu asusun ajiya a kullum.

Ya yabawa Hukumar NFIU bisa rawar da take takawa wajen gano kuɗaɗen ta’addanci, tare da bayyana cewa Ma’aikatar Shari’a, ofishin Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na ƙasa da sauran hukumomi suna aiki don tabbatar da an hukunta masu hannu a lamarin.

Wasu yan daba sun ajiye Makamansu a Kano

Ya kuma ce hukumomin tsaro suna bin diddigin wasu ‘yan siyasa da ake zargi suna tallafawa rashin tsaro domin amfanin kansu.

Najeriya na ci gaba da fama da matsalar ta’addanci musamman a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma, inda Boko Haram da ‘yan bindiga ke addabar jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wasu yan daba sun ajiye Makamansu a Kano

Gwamnatin Jihar Kano Hadin gwaiwa da Rundunar Yansandan Jihar...

Masu Mukamai a gwamnatin Kano ba su da uzurin kin taimakawa yan Kwankwasiyya – Sanusi Bature

Mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin...

Magoya bayan Barr Ibrahim Isa (Matawallen Gwagwarwa) sun aikawa Gwamnan Kano Budaddiyar Wasika

Daga Isa Ahmad Getso Kira don nemawa Barr. Ibrahim Isa...

Bukatun Nigeria da Tinubu ya mika a taron da ake yi a Japan

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya yi kiran samar da...