Muna kira ga INEC da ta sake duba sakamakon zaɓen Bagwai Da Shanono – Abdullahi Abbas

Date:

Jam’iyyar APC, reshen jihar Kano, ta bayyana cewa bata amince da sakamakon zaɓen cike gurbi na Dan Majalisar jihar da aka gudanar a ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, a mazabar Bagwai/Shanono.

“An samu maguɗi mai yawa, tashin hankali da tsoratar da masu kada kuri’a, tare da keta doka da oda gaba ɗaya, inda aka hana magoya bayan APC damar yin zaɓe cikin kwanciyar hankali, yayin da ’yan daba su ka yi abun da suke so a yayin zaben”.

FB IMG 1753738820016
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban jam’iyyar na jihar Kano Abdullahi Abbas ya sanyawa hannu kuma aka aikowa da Kadaura24.

APC ta jaddada cewa tsarin da aka bi bai cika ka’idodin zaɓe, gaskiya da adalci ba, tare da bayyana abin da ya faru a matsayin wani shiri na kwace ikon jama’a.

Dalilan da suka sa Kwankwaso ba zai hada hanya da Tinubu a zaben 2027 ba – Buba Galadima

Jam’iyyar ta yi kira ga hukumar zabe da ta gaggauta sake duba tsarin zaben da kuma sakamakon zaɓen, sannan ta na roƙon INEC da ta binciki rahotannin maguɗin da aka rika yadawa, tare da ɗaukar matakan da suka dace domin dawowa da al’umma kwarin gwiwar cigaba da amincewar da tsarin zaben Kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nan gaba kadan za mu bayyana sunayen masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya – Babban Hafsan tsaro

Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya ce...

Wasu yan daba sun ajiye Makamansu a Kano

Gwamnatin Jihar Kano Hadin gwaiwa da Rundunar Yansandan Jihar...

Masu Mukamai a gwamnatin Kano ba su da uzurin kin taimakawa yan Kwankwasiyya – Sanusi Bature

Mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin...

Magoya bayan Barr Ibrahim Isa (Matawallen Gwagwarwa) sun aikawa Gwamnan Kano Budaddiyar Wasika

Daga Isa Ahmad Getso Kira don nemawa Barr. Ibrahim Isa...