Rundunar yan sanda ta Sanya dokar takaita zurga-zurga a wasu kananan hukumomi a kano

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar Kano ta Sanya dokar takaita zurga-zurga a kananan hukumomin Ghari da Tsanyawa da kuma Bagwai da shanono, inda za a gudanar da zaben cike gurbi a ranar asabar mai zuwa .

” Dokar za ta Fara aiki daga 12 na daren Ranar juma’a har zuwa karfe 06 na yammacin Ranar Asabar 17 ga watan Augusta, 2025, an haramtawa kowa yawo da makami ko wata alamar jam’iyya a ranar zaben”.

FB IMG 1753738820016
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya Sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Ya ce Rundunar ta shirya tsaf domin Samar da ingantaccen tsaro a wadancan kananan hukumomin da za a gudanar da zaben .

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

Sanarwar ta ce Rundunar zata hada Kai da dukkanin hukumomin tsaro dake jihar Kano don tabbatar da an yi zaben cikin kwanciyar hankali da lumana.

Kiyawa ya ce Rundunar ta kuma haramtawa yan KAROTA da yan vigilante da Shiga cikin aikin Samar da tsaro a kananan hukumomin da za a gudanar da zaben .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Jam’iyyar APC ta bayyana matsayarta kan zaben cike gurbi a Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zabe:An kama ƴandaba sama da 100 da ake zargi da yunkurin tada tarzoma a Kano – INEC

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta...

Gwamnan Bauchi ya nada ɗan ƙasar China a matsayin mai bashi shawara kan tattalin arziƙi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya nada Mista Li...

Gwamnati da Malamai a Kano sun fitar da mafi karanci kudin sadaki da Zakka da Diyar Rai

Daga Kamal Yakubu Ali   Hukumar Zakka da Hubusi da Takwararta...