Sanya mata a shugabanci zai taimaka wajen kawo cigaba ga al’umma – NAWOJ Kano

Date:

Kungiyar mata ‘yan jarida ta Najeriya (NAWOJ), reshen jihar Kano, ta jaddada kudirinta na ganin ana Sanya mata a matakan shugabanci don su ba da ta su gudunmawar wajen kawo cigaba ga al’umma.

Da take jawabi a wajen wani taron karawa juna sani na yini gudu shugabar kungiyar Kwamared Bahijja Kabara ta jaddada cewa dole ne a baiwa mata ‘yancin bayar da gudunmuwarsu don kawo ci gaba ga al’umma.

FB IMG 1753738820016
Talla

Taron wanda aka shirya tare da hadin guiwar gidauniyar Aminu Magashi da kungiyar kula da lafiya da bincike ta al’umma, an shirya shi ne domin kara karfafa gwiwar mata ‘yan jarida wajen bayar da rahotanni na hakika kuma a kan lokaci, tare da magance kalubalen da suke fuskanta a cikin gida da ma duniya baki daya.

Gwamnan Kano ya raba tallafin kayan sana’o’i ga matasa 1130

Bahijja Kabara ta bukaci mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da suka samu don ciyar da aikinsu gaba da kuma muradun mata.

Ta yabawa gidauniyar Aminu Magashi bisa jajircewa da take yi wajen kula da lafiyar mata da yara, da kuma jin dadin al’umma, inda ta bayyana gidauniyar wacce za su cigaba da hada Kai tsare- don cigaban al’umma.

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

Kabara ya kuma yabawa Shugaban kungiyar NUJ na jihar Kano Kwamared Sulaiman Abdullahi Dederi bisa jagorancinsa na ci gaba da kuma yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa yadda yake ba da fifiko ga ci gaban mata musamman ta hanyar samar da dokar da kula da mata masu juna biyu kyauta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya raba tallafin kayan sana’o’i ga matasa 1130

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya raba tallafin...

‎2027: Tsohon SSG Na Kaduna Ya Shawarci Sha’ban Ya Bar APC Ya Shiga ADC Don Yin Takarar Gwamna

Daga Rahama Umar Kwaru ‎ ‎ ‎Wani bidiyo da ya fara yawo...

Allah ya yi wa Kanal Daudu Sulaimanu Rasuwa

Daga Jafar Adam   Allah ya yiwa Kanal Daudu Sulaiman Rasuwar...

Belin Dilan Kwaya: Gwamnan Kano ya kori wasu Hadimansa

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano karkashin Alhaji Abba...