Gwamnan Kano ya raba tallafin kayan sana’o’i ga matasa 1130

Date:

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya raba tallafin kayan sana’a ga matasa 1130 da aka yaye a makarantun koyar da sana’o’i shida da gwamnati ta bude.

Da yake jawabi a wajen rabon kayan tallafin a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati, gwamna Abba Kabir Yusuf yace gwamnatinsa ta himmatu wajen samarwa matasa ayyukan yi domin su dogara da kawunansu.

FB IMG 1753738820016
Talla

Daliban su 1130 sun fito ne daga makarantar koyar da kiwon Kifi data koyar da ilimin kwamfuta data koyar da kiwon dabbobi data koyar da ilimin kula da tssirrai data koyar da tukin mota da kuma ta koyar da wasan kwaikwayo.

Da yake jawabi ga matasan da aka yaye gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnati ta bawa daliban kwalejin nazarin ilimin kwamputa laptop da kunshin kayan gyaran computer da wayoyin hannu da kuma kudi naira dubu hamsin.

‎2027: Tsohon SSG Na Kaduna Ya Shawarci Sha’ban Ya Bar APC Ya Shiga ADC Don Yin Takarar Gwamna

Sai na ma makarantar koyon kiwon dabbobi wadanda suka samu tallafin shanu yayin da na makarantar koyon tukin mota suka rabauta da shaidar tuki (Driving licence) da kuma kudi Naira dubu 100 kowannensu.

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

Daliban kwalejin nazarin ilimin tsirrra kuwa, gwamna Abba Kabir Yusuf ya gwangwaje su da kayan aikin noma da tallafin kudi yayin da na makarantar koyon wasan kwaikwayo suka rabauta da camerar daukar hoto ta zamani da kuma kudi Naira dubu 50.

Ya yi kira ga matasan suyi kyakkyawan amfani da tallafin da kuma ilimin da suka Koya Yadda ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sanya mata a shugabanci zai taimaka wajen kawo cigaba ga al’umma – NAWOJ Kano

Kungiyar mata ‘yan jarida ta Najeriya (NAWOJ), reshen jihar...

‎2027: Tsohon SSG Na Kaduna Ya Shawarci Sha’ban Ya Bar APC Ya Shiga ADC Don Yin Takarar Gwamna

Daga Rahama Umar Kwaru ‎ ‎ ‎Wani bidiyo da ya fara yawo...

Allah ya yi wa Kanal Daudu Sulaimanu Rasuwa

Daga Jafar Adam   Allah ya yiwa Kanal Daudu Sulaiman Rasuwar...

Belin Dilan Kwaya: Gwamnan Kano ya kori wasu Hadimansa

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano karkashin Alhaji Abba...